Ƙasar Benin ta fuskanci tashin hankali a cewar Shugaban kasar Talon

 



Bayan shafe sa'o'i ba tare da an ji ɗuriyarsa ba, shugaban ƙasar Benin Patrice Talon ya bayyana a kafar talabijin inda ya yi wa al'ummar ƙasar jawabi, tare da bayyana cewa an daƙile yunƙurin juyin mulki da wasu sojoji suka yi a ƙasar.

Gwamnati ta ce ta daƙile yunƙurin juyin mulki da wasu sojoji suka so su yi, awanni bayan wasu gungun sojoji sun bayyana cewa sun karɓe iko da ƙasar.

Ya ce "yanzu an shawo kan lamarin baki ɗaya" bayan yunƙurin da masu juyin mulki suka yi tun da farko.

"Ina so na yaba wa jajricewar da sojojinmu da jagororinsu suka nuna, waɗanda suka... ci gaba da zama masu biyayya ga ƙasa," in ji Patrice Talon wanda ya bayyana a kafar talabijin ba tare da alamar tashin hankali ba.

"Gaba ɗayanmu mun tsaya tsayin daka, muka sake karɓo yankunanmu sannan muka kakkaɓe wuraren da masu cin amana suka ja daga.

"Wannan jajircewa ta ba mu damar yin galaba a kan waɗannan mutane, sannan muka kare ƙasarmu daga faɗawa cikin annoba," kamar yadda Shugaba Talon ya bayyana.


Comments

Popular posts from this blog

Yarjejeniyar Tsagaita Wuta a Syria: Sabon Matakin Diflomasiyya tsakanin Gwamnati da Mayaƙan Ƙurɗawa

Wani ɗan asalin Ireland ya shiga rikici a wata ƙasa – Gwamnatin Ireland na sa ido kan lamarin

Saudi Arabia da Najeriya Sun Kulla Yarjejeniyar Daukar Ma’aikata